Rundunar ‘yan sandan jihar Bayelsa ta bayyana a ranar Juma’ar da ta gabata cewa, ta tasa keyar wasu mutane biyu a gidan yari biyo bayan kama su da laifin mamaye babbar kotun jihar a ranar Laraba.
Wasu ‘yan daba da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne sun hargitsa zaman kotun da mai shari’a, Nayai Aganaba ke jagoranta a shari’ar da ake tafkawa a unguwanni da kananan hukumomi da kuma ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar APC a jihar.
Rundunar, a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Asinim Butswat ya fitar ranar Juma’a, ta bayyana wadanda ake zargin Promise Ogilogi da Azibabin Adiki.
Kwamishanan ‘yan sandan jihar Bayelsa, CP Ben Nebolisa Okolo, fdc, ya tuhumi jami’an ‘yan sanda da su kamo wadanda ake zargi da guduwa, sannan ya yi gargadin babu shakka cewa, rundunar ta shirya tsaf domin tunkarar duk wani mutum ko kungiyar da ta boye mutane, domin kawo cikas ga zaman lafiya da ake samu a jihar.