Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi sun tarwatsa zanga-zangar neman zaben #Endbad a jihar.
Rahoto na cewa jami’an ‘yan sanda sun harba barkonon tsohuwa kan masu zanga-zangar a ranar Alhamis, wadanda suka taru a kofar fadar Sarkin Bauchi.
Masu zanga-zangar dai na neman ganawa da sarkin ne amma shingen ‘yan sanda ya hana su.
Yayin da masu zanga-zangar suka dage kan ganawa da sarkin, jami’an ‘yan sanda sun baza barkonon tsohuwa domin tarwatsa su.