fidelitybank

An tabbatar da kashe mutane 25 tare da sace da dama a Katsina

Date:

Akalla mutane 25 aka hallaka, sannan aka sace wasu da dama a lokacin da ƴanbindiga suka kai hari a wani ƙauyen a jihar Katsina, a cewar hukumomi.

Gwamman ƴanbindigar sun isa ƙauyen Yargoje da ke ƙaramar hukumar Ƙankara a ranar Lahadi da daddare ne, kamar yadda kwamishinan tsaro na jihar, Nasiru Babangida Mu’azu, ya shaida wa BBC Hausa.

Mazauna ƙauyen sun ce maharan sun dinga harbin kan mai uwa da wabi, yayin da suka fasa shaguna tare da sace mutanen da kawo yanzu ba a san adadinsu ba.

Sai dai wasu rahotanni na cewa ƴanbindigar sun kashe fiye da mutane 50 tare da jikkata kimanin wasu 30.

A watan Disamba 2020, wasu ƴanbindiga sun sace ɗaliba 300 daga wata makarantar sakandare ta kwana ta maza da ke wajen Ƙankara, amma daga bisani aka sake su.

Matsalar ƴanfashin daji matsala ce da ta daɗe tana addabar jihar ta Katsina da wasu jihohin arewa-maso-yammacin ƙasar, duk da ƙoƙarin da hukumomi ke cewa suna yi domin magance matsalar.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp