Gwamnatin jihar Ondo ta ayyana makokin kwana uku domin alhinin mutuwar Rotimi Akeredolu wanda ya rasu da sanyin safiyar jiya, Laraba.
Mutuwar Akeredolu ta sa aka rantsar da mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa a matsayin gwamna.
Sabon gwamnan ya ba da umarnin sassauto da tutocin Najeriya a sassan jihar domin jimamin mutuwar marigayin.
Matakin na ƙunshe ne cikin sanarwar da babban sakataren yaɗa labaran gwamnan, Ebenezer Adeniyan ya fitar.
Akeredolu ya rasu yana da shekara 67, bayan ya shafe lokaci yana fama da cutar kansar jini da ta mafitsara.


