fidelitybank

An shawarci Tinubu ya kulla alaka da Rasha wajen farfado da tattalin arziki

Date:

An shawarci gwamnatin shugaba Ahmad Bola Tinubu da ta kara mai da hankali kan dangantakarta da kasar Rasha domin farfado da tattalin arzikin kasar.

A wata hira da manema labarai a Kano, fitaccen dan siyasar nan, Muhammadu Gambo Danpass, ya ce a fili yake cewa Jamhuriyar Rasha ta fi kowace kasa a yammacin duniya tsarin farfado da tattalin arzikin kasashen Afirka.

Danpass ya ce taron kasashen Afirka/Rasha da aka kammala kwanan nan da kuma sakamakonsa sun tabbatar da cewa Rasha ta fi daukar hankali wajen farfado da nahiyar Afirka.

Ya ce rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro da kasashen Afirka sama da 40 da Rasha ta yi, ya nuna cewa kasar na nufin zaman lafiya ga nahiyar fiye da sauran wadanda ke sayar da harsashi ga bakar fata don yaki.

“Saboda haka, ya kamata Shugaba Bola Tinubu ya kara ba da muhimmanci ga dangantakarmu da Rasha, domin gwamnatinsa ta gaggauta farfado da tattalin arziki don amfanin al’umma”.

Danpass wanda jigo ne a akidar Kwankwasiyya ta Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce gwamnatinsu a Kano nan gaba kadan za ta kara daukaka jihar.

Ya kuma yi kira ga ‘yan kasa da su yi hakuri da gwamnati domin nan ba da dadewa ba abubuwa za su daidaita.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp