fidelitybank

An shawarci Buhari kan maida hankali ga noman auduga da gina masana’antu

Date:

Masu ruwa da tsaki a bangaren auduga, masaku da sutura a Najeriya, sun bukaci gwamnati da ta aiwatar da manufar taswirar masana’antu, wanda a ganinsu, yana da matukar muhimmanci ga farfado da fannin.

Shugaban kungiyar auduga ta kasa (NACOTAN), Achimugwu Anibe, ya ce, aiwatar da manufar zai kuma inganta alaka tsakanin masu ruwa da tsaki.

Masu ruwa da tsaki sun gana a wani taron karawa juna sani na kwana daya a Abuja, inda suka tattauna manufar CTG. Sun bayyana bukatar kara bunkasa noman auduga, karfin masana’antar ginshi da masaku a kasar.

An gudanar da taron ne tare da taimakon hukumar hadin gwiwa ta Jamus Deutsche Zusammennarbett, Tarayyar Turai (EU) da ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta Najeriya.

Sauran manyan masu ruwa da tsaki sun hada da kungiyar dillalan auduga ta Najeriya (COPMAN), kungiyar masu sana’ar kayan masarufi ta Najeriya (NTMA) da kuma Cotton Ginners (GAMAN).

Babban bankin kasa CBN a shekarar da ta gabata ya bayyana shirin farfado da fannin. Shirin dai shi ne zai baiwa kasar damar dogaro da kanta wajen noman auduga da kuma samar da ayyukan yi, tare da inganta kwarewar ‘yan Najeriya a kan darajar noman auduga.

A baya Najeriya na da kusan masana’anta 52, amma 21 ne kawai ke aiki a yanzu.

A sakamakon haka, ton 100 na auduga ne ake sarrafawa a duk shekara maimakon tan 600, inji Anibe.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp