fidelitybank

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Date:

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada, ya sasanta rikicin da aka shafe sama da shekaru 30 ana yi kan makarantar Islamiyya da masallacin Sharada.

An dauki lokaci mai tsaho ana wannan takaddamar tsakani Alhaji Shehu Uba Sharada da Dagacin garin Sharada Alhaji Iliyasu Ma’azu, da ya ke wakiltar al’ummar unguwar, da ta kai an kai kararraki sama da 100 a kotuna daban daban.

Taron sulhun ya gudana ne a daren Alhamis a gidan Hon. Sha’aban Sharada da aka shafe kimanin awanni 3 ana tattaunawa, da har ta kai an cimma matsaya da kuma samar da sulhu ga bangarorin biyu.

Dukkanin bangarorin sun yafi juna, yayinda suka tabbatar da cewa sabanin da ke tsakaninsu ya zo karshe. Kamar yadda Malam Sha’aban Ibrahim Sharada ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Zaman sulhun ya samu halartar wakilan bangarorin biyu, da bangaren masaurata karkashin jagorancin Dallatun Kano Hakimin Gundummar Sharada Malam Mahe Bashir, da kuma baturen ‘yansanda na chaji ofis din Sharada CSP. Abdurrahim Adamu, da ma sauran masu ruwa da tsaki na unguwar ta sharada

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp