Wasu da ba a san ko su waye ba sun kashe wani yaro mai suna Abdulkadir dan shekara 12 a Zariya.
Marigayi Abdulkadir, mazaunin Madarkaci, an ce ya gamu da ajalinsa ne a ranar Litinin, lokacin da aka tura shi ya karbi waya daga a wajen masu caji a kasuwanci da ke kusa, amma bai dawo ba.
A cewar mahaifinsa, Aminu Saleh Muhammad, an gano gawar Abdulkadir da aka yanke a wani gini da ba a kammala ba a yankin.
Wata majiya ta bayyana cewa mahaifin marigayin, Aminu, ya yi zargin cewa wadanda suka kashe shi ‘yan ibada ne, yana mai jaddada cewa, “sun yanka shi ne ta hanyar cire masa idanuwa, al’aurarsa, harshensa kuma suka karya masa kafarsa, tare da tsage masa kwanyarsa.”
Mahaifin ya nemi gawar daga hannun ‘yan sanda domin binne gawar.
An binne gawar yaron kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
DSP Muhammad Jalige, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya ce wasu da ba a san ko su wanene ba ne suka yanka yaron har lahira.
Jami’in hulda da jama’a ya ce, tuni ‘yan sanda suka fara bincike a kokarin ganowa tare da cafke wadanda suka aikata laifin domin fuskantar fushin doka.