fidelitybank

An sassara dan shekara 12 gunduwa-gunduwa a Zaria

Date:

Wasu da ba a san ko su waye ba sun kashe wani yaro mai suna Abdulkadir dan shekara 12 a Zariya.

Marigayi Abdulkadir, mazaunin Madarkaci, an ce ya gamu da ajalinsa ne a ranar Litinin, lokacin da aka tura shi ya karbi waya daga a wajen masu caji a kasuwanci da ke kusa, amma bai dawo ba.

A cewar mahaifinsa, Aminu Saleh Muhammad, an gano gawar Abdulkadir da aka yanke a wani gini da ba a kammala ba a yankin.

Wata majiya ta bayyana cewa mahaifin marigayin, Aminu, ya yi zargin cewa wadanda suka kashe shi ‘yan ibada ne, yana mai jaddada cewa, “sun yanka shi ne ta hanyar cire masa idanuwa, al’aurarsa, harshensa kuma suka karya masa kafarsa, tare da tsage masa kwanyarsa.”

Mahaifin ya nemi gawar daga hannun ‘yan sanda domin binne gawar.

An binne gawar yaron kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

DSP Muhammad Jalige, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya ce wasu da ba a san ko su wanene ba ne suka yanka yaron har lahira.

Jami’in hulda da jama’a ya ce, tuni ‘yan sanda suka fara bincike a kokarin ganowa tare da cafke wadanda suka aikata laifin domin fuskantar fushin doka.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp