Sakamakon tarzomar da ta tashi a lokacin zanga-zangar nuna rashin amincewa da tsadar rayuwa da aka gudanar a sassa daban daban na Najeriya a jiya alhamis, gwamnatin jihar Jigawa ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 har zuwa lokacin da al’amuran tsaro suka inganta.
Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi wanda ya bayanna haka ya ce sun É—auki wannan mataki ne sakamakon abubuwan da suka biyo baya a zanga zangar waÉ—anda suka haÉ—a da sace sace da lalata kayan hukuma.
Ita ma gwamnatin jihar Katsina ta sanya dokar hana fita na sa’o’i 24 a Æ™aramar hukumar Dutsima, yayinda ta hana zirga-zirgar mutane daga Æ™arfe bakwai na yamma zuwa Æ™arfe bakwai na safe a sauran Æ™ananan hukumomin 33 da ke jihar.