fidelitybank

An samu ƙaruwar cutar ƙyandar biri a Najeriya

Date:

Kwararru a fannin kiwon lafoya sun ce, an samu karuwar yaduwar cutar kyandar biri a Najeriya, inda yanzu ta bazu zuwa jihohi 26 ciki har da Abuja, babban birnin tarayyar kasar.

Jaridar Daily Trust, wadda ta rawaito wannan labari, ta kara da cewa kwararrun sun ce wannan lamari abin tsoro ne wanda yake bukatar ba shi kulawar da ta dace.

Ana daukar cutar ce daga dabbobi kuma ana yada ta a tsakanin mutane.

Tun daga farkon watan Janairun 2022 zuwa Augustan shekarar, an samu mutum 473 da ake zargi sun kamu da cutar, a in da aka tabbatar mutum 172 da suka kamu da ita a cikinsu.

Bayanan da aka samu daga hukumar kula da cutuka masu yaduwa ta kasar, NCDC, sun nuna cewa adadin wadanda suka kamu da cutar a 2022 kawo yanzu, ya fi na wanda aka samu a 2017 da 2018 da 2019 da 2020 da kuma na 2021.

Tun daga farkon shekarar 2022, kasashe da dama ke fuskantar bullar cutar ta kyandar biri, abin da ya sa shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Gebreyesus, ya ayyana dokar ta-baci a kanta a ranar 23 ga watan Yulin shekarar.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp