fidelitybank

An samu ‘yan takara 20 da ta’ammali da ƙwaya a Kano

Date:

Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun ƙwayoyi ta Najeriya ta ce ta samu ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin Kano 20 da laifin ta’ammali da ƙwaya bayan gwajin ƙwayoyin da aka yi musu.

Jaridar daily Trust ta ambato shugaban hukumar NDLEA na jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad, na cewa gwaji ya tabbatar da cewa wasu daga cikin ‘yan takarar – waɗanda jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar ta gabatar – an same su da laifin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

Ya ƙara da cewa hukumar na sa ra san kammala aikin tantance ‘yan takarar ta hanyar gwajin ƙwayar kafin wa’adin da aka ɗibar mata na kammala aikin.

Jam’iyyar NNPP ce dai ta buƙaci a yi wa duka ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin gwajin a wani abu da wasu ke kallo a matsayin matakin rage yawan ‘yan takarar.

Hukumar zaɓen jihar dai ta sanya ranar 26 ga watan Ocotober domin gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomin jihar 44 haɗe da kansiloli a mazaɓu 484.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...
X whatsapp