fidelitybank

An samu ‘yan takara 20 da ta’ammali da ƙwaya a Kano

Date:

Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun ƙwayoyi ta Najeriya ta ce ta samu ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin Kano 20 da laifin ta’ammali da ƙwaya bayan gwajin ƙwayoyin da aka yi musu.

Jaridar daily Trust ta ambato shugaban hukumar NDLEA na jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad, na cewa gwaji ya tabbatar da cewa wasu daga cikin ‘yan takarar – waɗanda jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar ta gabatar – an same su da laifin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

Ya ƙara da cewa hukumar na sa ra san kammala aikin tantance ‘yan takarar ta hanyar gwajin ƙwayar kafin wa’adin da aka ɗibar mata na kammala aikin.

Jam’iyyar NNPP ce dai ta buƙaci a yi wa duka ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin gwajin a wani abu da wasu ke kallo a matsayin matakin rage yawan ‘yan takarar.

Hukumar zaɓen jihar dai ta sanya ranar 26 ga watan Ocotober domin gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomin jihar 44 haɗe da kansiloli a mazaɓu 484.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp