fidelitybank

An samu ‘yan takara 20 da ta’ammali da ƙwaya a Kano

Date:

Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun ƙwayoyi ta Najeriya ta ce ta samu ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin Kano 20 da laifin ta’ammali da ƙwaya bayan gwajin ƙwayoyin da aka yi musu.

Jaridar daily Trust ta ambato shugaban hukumar NDLEA na jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad, na cewa gwaji ya tabbatar da cewa wasu daga cikin ‘yan takarar – waɗanda jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar ta gabatar – an same su da laifin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

Ya ƙara da cewa hukumar na sa ra san kammala aikin tantance ‘yan takarar ta hanyar gwajin ƙwayar kafin wa’adin da aka ɗibar mata na kammala aikin.

Jam’iyyar NNPP ce dai ta buƙaci a yi wa duka ‘yan takarar shugabannin ƙananan hukumomin gwajin a wani abu da wasu ke kallo a matsayin matakin rage yawan ‘yan takarar.

Hukumar zaɓen jihar dai ta sanya ranar 26 ga watan Ocotober domin gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomin jihar 44 haɗe da kansiloli a mazaɓu 484.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp