fidelitybank

An samu raguwar kashe mutane da sace su a cikin wata guda a Najeriya – Beacon

Date:

Najeriya ta samu raguwa a yawan mutanen da ake kashewa, da waɗanda ake garkuwa da su, da kuma ayyukan rashin tsaro a cikin watan Yuni, idan aka kwatanta da watan Mayu na shekarar da muke ciki ta 2024.

Hakan na ƙunshe ne cikin rahoton wata-wata na al’amuran tsaro da kamfanin Beacon Consulting mai nazari kan harkokin tsaro ya fitar a yau Litinin.

Rahoton ya ce: “A watan Yunin 2024 an samu raguwar kai hare-hare, inda aka kai hari sau 618. Wannan na nuna cewa an samu raguwar kai hare-hare da kashi 19.32 cikin 100 idan aka haɗa da hare-hare 766 da aka kai a watan Mayu”.

Haka nan rahoton ya nuna cewa an samu raguwar matsalar garkuwa da mutane a Najeriyar cikin watan na Yuni da kimanin kashi 58.59 cikin 100.

“An yi garkuwa da mutum 1,128 a watan Mayun 2024, yayin da a watan Yuni aka yi garkuwa da 467.”

A ɓangaren kashe-kashe kuwa, shi ma rahoton ya una cewa an samu raguwa da kashi 5.96 cikin 100.

“An kashe mutum 1,090 a watan Mayun 2024, inda a Yuni abin ya ragu zuwa 1,025 a watan Yuni.”

Harin ƙunar baƙin wake da ƙungiyar Boko Haram ta kai a garin Gwoza na jihar Borno, wanda ya kashe aƙalla mutum 30 a ƙarshen watan Yuni, ya ƙara fito da matsalar tsaro da ake fuskanta a sassa daban-daban na ƙasar.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta sha yin iƙirarin tarwatsa ƙungiyar.

Haka nan, ƴan fashin daji na cigaba da kai samame suna kashe mutane da garkuwa da su a jihohi kamar Zamfara, da Katsina, da Kaduna, a arewa maso yammacin ƙasar.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp