fidelitybank

An samu gagarumin sauyi a zaben baya – Gwamnatin Tarayya

Date:

Fadar gwamnatin ta ce, zabukan da aka yi na shugaban ƙasa da ‘yan majalisun dokoki na tarayya ranar 25 ga watan Fabarairu, gagarumin cigaba ne idan aka kwatanta da zaɓukan da aka yi a ƙasar a baya.

A wata sanarwa da kakakin shugaba Buhari, Mallam Garba Shehu ya fitar, fadar ta ce, duk da cewa an samu wasu matsaloli nan da can, wannan ba zai sa a ce zaɓen ya gaza ba.

Fadar shugaban ta nuna godiya kan damuwar da manyan jagororin masu sanya ido na ƙasashen waje suka nuna a kan matsalolin da aka samu kan kayan aiki a lokacin zaɓukan.

Buhari ya koma fadar gwamnati daga Daura

Sanarwar ta ce duk da ‘yan matsalolin da aka samu ba za a ce zaɓen ya gaza ba, illa dai waɗanda suka faɗi ne suke nuna gazawarsa.

Kakakin ya ce zaɓen na Najeriya ba shi kaɗai ba ne ake samun ire-iren waɗannan matsaloli abu ne da kusan a kowa ce ƙasa ake iya samu a zaɓe.

Ta nuna cewa ko ba komai yadda Ma’aikatar harkokin waje ta Amurka da Firaministan Birtaniya Rishi Sunak da sauran shugabannin Afirka ta Yamma da na Tarayyar Afirka suka taya murna ga dan takarar APC Bola Ahmed Tinubu, wanda ya yi nasara a wannan zaɓe da ya kasance wanda aka fi fafatawa a tarihin Najeriya, hakan ya nuna cewa abin a yaba ne.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp