Fadar gwamnatin ta ce, zabukan da aka yi na shugaban ƙasa da ‘yan majalisun dokoki na tarayya ranar 25 ga watan Fabarairu, gagarumin cigaba ne idan aka kwatanta da zaɓukan da aka yi a ƙasar a baya.
A wata sanarwa da kakakin shugaba Buhari, Mallam Garba Shehu ya fitar, fadar ta ce, duk da cewa an samu wasu matsaloli nan da can, wannan ba zai sa a ce zaɓen ya gaza ba.
Fadar shugaban ta nuna godiya kan damuwar da manyan jagororin masu sanya ido na ƙasashen waje suka nuna a kan matsalolin da aka samu kan kayan aiki a lokacin zaɓukan.
Buhari ya koma fadar gwamnati daga Daura
Sanarwar ta ce duk da ‘yan matsalolin da aka samu ba za a ce zaɓen ya gaza ba, illa dai waɗanda suka faɗi ne suke nuna gazawarsa.
Kakakin ya ce zaɓen na Najeriya ba shi kaɗai ba ne ake samun ire-iren waɗannan matsaloli abu ne da kusan a kowa ce ƙasa ake iya samu a zaɓe.
Ta nuna cewa ko ba komai yadda Ma’aikatar harkokin waje ta Amurka da Firaministan Birtaniya Rishi Sunak da sauran shugabannin Afirka ta Yamma da na Tarayyar Afirka suka taya murna ga dan takarar APC Bola Ahmed Tinubu, wanda ya yi nasara a wannan zaɓe da ya kasance wanda aka fi fafatawa a tarihin Najeriya, hakan ya nuna cewa abin a yaba ne.