fidelitybank

An samu asarar rayuka 182 a Kano cikin shekarar 2021 – Hukumar kashe gobara

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce sama da kadarori na Naira miliyan 660 ne suka salwanta a gobarar da ta afku a fadin jihar a shekarar 2021.

Jami’in hulda da jama’a na SFS, Saminu Yusuf Abdullahi, wanda ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai, ya ce an samu kiran kashe gobara 831 daga gidajen kashe gobara 27 a fadin jihar, inda ya ce jami’an hukumar sun kai daukin gaggawar ceto 818.

Abdullahi ya bayyana cewa daga watan Janairu zuwa Disamba, 2021, sun samu kira na karya 201.

Ya ce”Mutane 98 ne suka mutu daga jimillar mutane 113 da suka fada cikin tafki ko rafuka yayin da su ke ninkaya, akalla mutane 37 ne suka fada a cikin rijiya kuma daga adadin, 27 da abin ya shafa sun mutu”.

Abdullahi ya yi nuni da cewa, a lokuta daban-daban, an yi asarar rayuka 182 daga watan Janairu zuwa Disamba 2021.

Ya bayyana cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar sun ceci kadarorin da ya kai N1, 579,706,274 daga watan Janairu zuwa Disamba, 2021.

A cewarsa, a lokacin damina ta shekarar da ta gabata, an samu rugujewar gini guda biyu, inda aka ceto mutum daya da wutar lantarkin ta kama a gidan titin jirgin na Kofar Nassarawa.

Ya ce, Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Alhaji Hassan Ahmad Muhammad Muhammad ya shawarci jama’a da su kula sosai da kayayyakin wuta domin gujewa tashin gobara.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp