fidelitybank

An samu asarar rayuka 182 a Kano cikin shekarar 2021 – Hukumar kashe gobara

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce sama da kadarori na Naira miliyan 660 ne suka salwanta a gobarar da ta afku a fadin jihar a shekarar 2021.

Jami’in hulda da jama’a na SFS, Saminu Yusuf Abdullahi, wanda ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai, ya ce an samu kiran kashe gobara 831 daga gidajen kashe gobara 27 a fadin jihar, inda ya ce jami’an hukumar sun kai daukin gaggawar ceto 818.

Abdullahi ya bayyana cewa daga watan Janairu zuwa Disamba, 2021, sun samu kira na karya 201.

Ya ce”Mutane 98 ne suka mutu daga jimillar mutane 113 da suka fada cikin tafki ko rafuka yayin da su ke ninkaya, akalla mutane 37 ne suka fada a cikin rijiya kuma daga adadin, 27 da abin ya shafa sun mutu”.

Abdullahi ya yi nuni da cewa, a lokuta daban-daban, an yi asarar rayuka 182 daga watan Janairu zuwa Disamba 2021.

Ya bayyana cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar sun ceci kadarorin da ya kai N1, 579,706,274 daga watan Janairu zuwa Disamba, 2021.

A cewarsa, a lokacin damina ta shekarar da ta gabata, an samu rugujewar gini guda biyu, inda aka ceto mutum daya da wutar lantarkin ta kama a gidan titin jirgin na Kofar Nassarawa.

Ya ce, Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Alhaji Hassan Ahmad Muhammad Muhammad ya shawarci jama’a da su kula sosai da kayayyakin wuta domin gujewa tashin gobara.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp