fidelitybank

An samu ƙaruwar rashin tsaro a Najeriya a watan Mayu

Date:

Wani rahoto da kamfanin Beacon Consulting ya fitar ya nuna cewa an samu karuwar rashin tsaro a watan Mayun 2024 da kashi 10.28 inda aka samu faruwar al’amura da ke nuna taɓarɓarewar tsaro sau 762, idan aka kwatanta ta watan Afrilun da ya gabata da al.amuran rashin tsaro suka faru sau 691.

” Wattan Mayun 2024 ya gano yadda rashin tsaro ya ƙara ƙamari inda ya ƙaru da kaso 262.70 saboda samun ƙaruwar garkuwa da mutane. Ana kuma alaƙanta hakan ne sakamakon hare-haren ƴan bindiga a arewa maso yammacin ƙasar….” In ji rahoton.

To sai dai rahoton ya nuna cewa duk da samun ƙarin matsalolin tsaro da aka samu a watan Mayun amma kuma an samu ragin yawan mace-mace a watan inda alƙaluman suka ragu zuwa 1090 daga 1097 a watan Afrilu.

Hakan in ji rahoton na nuna raguwar mace-macen ne da kaso 0.64.

Rahoton ya kuma lissafa jihohin da aka fi samun matsalolin da suka haɗa da Borno da Edo da Abuja da Kaduna da Katsina da Kogi da Kwara da Niger da Sokoto da kuma Zamfara.

Daga ƙarshe rahoton ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su ɗauki dukkannin matakan da suka kamata wajen ganin an kare dukiya da rayukan al’umma.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp