fidelitybank

An samu ƙaruwar yunwa a Najeriya – Ƙungiyar Amnesty

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Amnesty International, ta ce, an samu ƙaruwar yunwa da take hakkin bil adama a Najeriya da wasu ƙasashen Afirka.

A cikin rahoton da ƙungiyar ke fitarwa shekara-shekara ta bayyana irin tasirin tashe-tashen hankula a mafi yawan ƙasashen Afirka kudu da hamadar sahara, inda ta ɗora alhakin hakan kan rashin ingantaccen shugabanci da ƙungiyoyin duniya.

Rahoton ya ce a nahiyar Afirka ‘yan jarida da masu rajin kare hakkin bil adama da ‘yan adawar siyasa na fuskantar danniya a ƙasashe irinsu Kamaru da Ethiopia da Eswatini da Guinea da Mali da Mozambique da Senegal da kuma Zimbabwe.

Haka kuma rahoton ya ce ”an samu mace-macen masu zanga-zanga da ƙungiyar ta alaƙanta da amfani da ƙarfi fiye da kima da jami’an tsaro ke yi wa masu zanga-zanga a ƙasashen Najeriya da Chadi da Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo da Guinea da Kenya da Senegal da Sierra Leone da Somalia da Sudan, da wasu ƙasashe.”

Amnesty International ta kuma nuna cewa rashin hukunta masu take haƙƙin bil adama ya ƙara rura rikice-rikice awasu ƙasashen Afirka. In ji BBC.

Rahoton ya kuma ambato raunin ƙungiyoyin duniya ciki har da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyar Tarayyar Afirka wajen kasa magance laifukan take haƙƙin bil adama da aka aikata ƙarƙashin dokokin duniya a ƙasashe irin su Myanmar da Yemen,da wasu ƙasashen nahiyar Afirka da suka haɗar da Ethiopia da Burkina Faso da kuma Sudan ta Kudu.

”Rikice-rikice, da ƙarancin abinci – wanda yaƙin Ukraine ya haddasa da ɗumamayar yanayi – sun kawo cikas wajen yunƙurin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasashen duniya da annobar korona ta haddasa”, in ji rahoton

Kan haka ne rahoton ya ce an take ‘yancin miliyoyin mutane na samun abinci, da lafiya da samun ingantacciyar rayuwa a faɗin ƙasashen Africa.

Domin kuwa a cewar rahoton”mamayar da Rahsa ke yi wa Ukraine ta kawo nakasu wajen samun alkama a mafi yawan ƙasashen Afirka da suka dogara da alkamar ƙasashen biyu.

Sannan tashin farashin makamashi ya haddasa tashin farashin kayan abinci a ƙasashen na Afirka, kamar yadda rahoton ya bayyana

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp