Koriya ta Kudu ta ce an sako wasu ‘yan ƙasarta biyu da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Najeriya kusan makonni uku da suka gabata.
Ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce an samu ceto mutanen ne sakamakon haɗin gwiwa tsakanin kamfaninsu na Daewoo Engineering and Construction da kuma hukumomin Najeriya.
Sai dai babu bayanai kan cewa ko sai da aka biya kuɗin fansa kafin kuɓutar da su ba.
A lokacin da aka zo sace mutanen kimanin mako uku da suka wuce, an kashe sojojin Najeriya huɗu da ke gadinsu, tare da wasu direbobi biyu.