fidelitybank

An saki Gwarzonnmahaddacin Alkur’ani na ƙasa bayan an kashe shugaban ƴan Bindiga

Date:

A Najeriya, iyalan mahardacin Alkur’anin nan da ƴanbindiga suka sace a jihar Katsina tare da mahaifinsa sun ce sun kuɓuta daga hannun masu garkuwa da su.

Kimanin mako biyu da suka wuce ne dai aka sace Alaramma Abdulsalam Rabi’u Faskari, wanda ya zama gwarzon gasar karatun Alƙur’ani mai girma ta ƙasa da aka yi a jihar Kebbi tare da mahaifinsa da ƴanuwansa bayan gwamna jiharsa ta Katsina ya karrama shi.

Malam Rabiu Zakariya Faskari, shi ne mahaifinsa da aka sace su tare a yankin Faskari, ya bayyana wa BBC cewa sun tsira ne ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Ya ce asali a Katsina ne ƴanbindiga suke riƙe da su, sai ƙasurgumin ɗanbindiga, Yellow ya zo daga Zamfara, ya “ƙwace mu da ƙarfin tsaiya daga inda muke. Sai da ya musu dukan tsiya kafin ya tafi da mu,” in ji shi.

Ya ce an yi ciniki, amma ɗanbindigar ya ƙi amicewa. “Haka muka cigaba da zama muna addu’a, sannan ana yi mana addu’a. Sai ranar Juma’a kawai aka zo aka ce mana mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauko mu suka tsallako da mu dajin Munhaye suka kawo wani gari suka ajiye mu. Daga garin sai da muka yi tafiya ta awa huɗu.”

Ya ce da suka hau babur ne shi ne ɗan acaɓa ke faɗa musu an kashe shugaban dabar mai suna Yellow, “ashe shi ya sa yaransa suka sake mu muka tafi.”

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp