fidelitybank

An saki Gwarzonnmahaddacin Alkur’ani na ƙasa bayan an kashe shugaban ƴan Bindiga

Date:

A Najeriya, iyalan mahardacin Alkur’anin nan da ƴanbindiga suka sace a jihar Katsina tare da mahaifinsa sun ce sun kuɓuta daga hannun masu garkuwa da su.

Kimanin mako biyu da suka wuce ne dai aka sace Alaramma Abdulsalam Rabi’u Faskari, wanda ya zama gwarzon gasar karatun Alƙur’ani mai girma ta ƙasa da aka yi a jihar Kebbi tare da mahaifinsa da ƴanuwansa bayan gwamna jiharsa ta Katsina ya karrama shi.

Malam Rabiu Zakariya Faskari, shi ne mahaifinsa da aka sace su tare a yankin Faskari, ya bayyana wa BBC cewa sun tsira ne ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Ya ce asali a Katsina ne ƴanbindiga suke riƙe da su, sai ƙasurgumin ɗanbindiga, Yellow ya zo daga Zamfara, ya “ƙwace mu da ƙarfin tsaiya daga inda muke. Sai da ya musu dukan tsiya kafin ya tafi da mu,” in ji shi.

Ya ce an yi ciniki, amma ɗanbindigar ya ƙi amicewa. “Haka muka cigaba da zama muna addu’a, sannan ana yi mana addu’a. Sai ranar Juma’a kawai aka zo aka ce mana mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauko mu suka tsallako da mu dajin Munhaye suka kawo wani gari suka ajiye mu. Daga garin sai da muka yi tafiya ta awa huɗu.”

Ya ce da suka hau babur ne shi ne ɗan acaɓa ke faɗa musu an kashe shugaban dabar mai suna Yellow, “ashe shi ya sa yaransa suka sake mu muka tafi.”

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp