fidelitybank

An saki daliban jami’ar Wukari daga hannun ‘yan ta’adda

Date:

Ɗalibai biyu daga jami’ar gwamnatin tarayya ta Wukari da ke jihar Taraba da ake zargin masu garkuwa sun sace su sun shaƙi iskar ƴanci.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa, an saki ɗaliban ranar Alhamis da daddare a kusa da ƙauyen Chinkai da ke ƙaramar hukumar Wukari.

Shugabar sashen yaɗa labarai na jami’ar, Ashu Agya ce ta bayyana hakan ga Channels ta wayar tarho.

A cewarta an biya kuɗin fansa kafin sakin ɗaliban.

Tun farko kafar yaɗa labaran ta ruwaito cewa an sace ɗaliban da ƙarfe 10 na dare ranar 1 ga watan Afrilu a wani wajen cin abinci da ke wajen harabar makarantar.

A ranar da lamarin ya faru, masu garkuwar sun yi ƙoƙarin sace wasu ɗaliban sai dai ba su yi nasara ba abin da ya janyo suka lakaɗawa ɗaliban da masu shagon duka tare da sace kayansu.

Kashi 90 cikin 100 na malamai da ɗaliban makarantar na zama ne a wajen jami’ar kamar yadda shugaban jami’ar ya faɗa a bikin yaye ɗalibai da aka yi a baya-bayan nan.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp