fidelitybank

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta ce ta sake karɓar ‘yan ƙasar 294 a ranar Litinin da aka kwaso daga maƙwabciyarta Jamhuriyar Nijar.

Wata sanarwa daga hukumar ta ce jirgi biyu ne ya kwaso mutanen daga garin Agadez na Nijar zuwa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano ne da ke Kano bayan sun maƙale a can.

Ta ce jirgin farko ya sauka ne da misalin ƙarfe 1:30 ɗauke da mutum 148, na biyun kuma ya sauka da mutum 146 da misalin ƙarfe 4:29 na yamma.

Bayanai sun nuna akasarin mutanen kan maƙale ne bayan yin zango a Agadez yayin da suke kan hanyarsu ta kaiwa ƙasashen Aljeriya ko Libya ko kuma nahiyar Turai.

Ƙungiyoyin bayar da agaji na ƙasashen duniya ne ke taimakawa tare da hadin gwiwar gwamnati wajen mayar da su gida a jirgi.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp