Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki kan wasu mutane a jihar Neja, tare da hallaka mutane da dama a yankunan.
Jaridar Daily Trust ta tahoto cewa, akalla mutane takwas ne aka kashe, yayin da aka sace 14 da suka hada da mata biyar a kauyukan Gpekure, Makuba da Galapai a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja.
Rahotanni sun nuna cewa, mutanen yankin sun kasance cikin farmakin ‘yan ta’adda tun daren Juma’a da suka fara kai hari a Gpekure, inda suka kashe mutane bakwai tare da sace wasu bakwai.
Hare-haren sun tilastawa mazauna yankin da dama, musamman mata da yara yin gudun hijira zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira da ke Zumba da Gwada da kuma makarantar Sakandare ta Gwamnati (GDSS) da ke Shiroro.
Wani mazaunin garin ya shaida cewa, an kai hari a Gpekure da Makuba da misalin karfe 11 na daren ranar Asabar, yayin da na Galapai aka kai harin da misalin karfe 1:00 na ranar Lahadi.