fidelitybank

An sake kubutar da ‘yar Chibok a jihar Borno

Date:

Sojoji ƙarƙashin rundunar kakkaɓe dazuka daga ƴan ta’adda a yankin arewa maso gabas sun kuɓutar da ƙarin ƴar makarantar Chibok, Lydia Smith.

Rahotanni daga jaridun Najeriya na cewa sojojin runduna ta 82 a ƙaramar hukumar Gwoza sun kuɓutar da Lydia ne tare da ƴaƴanta uku a ranar Laraba.

Jaridun sun ruwaito cewa Lydia ta miƙa wuya ga dakarun a Gwoza. Tana ɗauke da juna biyu da ya kai wata biyar kuma ta yi iƙirarin cewa ta fito daga garin Pemi a Chibok.

A ranar 14 ga watan Afrilu ne aka cika shekara 10 tun bayan da Boko Haram ta sace ƴan matan su 276 daga makarantarsu da ke Chibok a jihar Borno.

57 daga cikin ɗaliban sun kuɓuta byan sace su, 16 kuma an kuɓutar da su daga bisani sai wasu 107 da aka sake su a lokuta daban-daban bayan da aka tattauna.

Gwamnati da sojojin Najeriya sun yi alƙawarin ƙwato ragowar ƴan matan da har yanzu suke hannun mayaƙan na Boko Haram.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp