fidelitybank

An sake kubutar da ‘yar Chibok a jihar Borno

Date:

Sojoji ƙarƙashin rundunar kakkaɓe dazuka daga ƴan ta’adda a yankin arewa maso gabas sun kuɓutar da ƙarin ƴar makarantar Chibok, Lydia Smith.

Rahotanni daga jaridun Najeriya na cewa sojojin runduna ta 82 a ƙaramar hukumar Gwoza sun kuɓutar da Lydia ne tare da ƴaƴanta uku a ranar Laraba.

Jaridun sun ruwaito cewa Lydia ta miƙa wuya ga dakarun a Gwoza. Tana ɗauke da juna biyu da ya kai wata biyar kuma ta yi iƙirarin cewa ta fito daga garin Pemi a Chibok.

A ranar 14 ga watan Afrilu ne aka cika shekara 10 tun bayan da Boko Haram ta sace ƴan matan su 276 daga makarantarsu da ke Chibok a jihar Borno.

57 daga cikin ɗaliban sun kuɓuta byan sace su, 16 kuma an kuɓutar da su daga bisani sai wasu 107 da aka sake su a lokuta daban-daban bayan da aka tattauna.

Gwamnati da sojojin Najeriya sun yi alƙawarin ƙwato ragowar ƴan matan da har yanzu suke hannun mayaƙan na Boko Haram.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp