fidelitybank

An sake gano gawarwaki 54 da suka nutse a kogin Neja

Date:

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya ta ce ta gano aƙalla gawarwaki 54 a wurin da hatsarin kwale-kwalen jihar Kogi ya auku ranar Juma’ar da ta gabata.

Ana dai kyautata zaton cewa har yanzu ba a ga fiye da mutum 100 ba, yayin da aka ceto wasu 24 da ransu.

Ƙwararrun ninƙaya da masu iyo na ci gaba da neman sauran mutanen, sai dai fatan samun ragowar mutanen da rai na ci gaba da raguwa a zukatan al’umma.

Kwale-kwalen ɗauke da fasinjoji fiye da 200 ya kife a cikin ruwan Kogin Neja tsakanin jihohin Kogi da Neja da ke tsakiyar Najeriya, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa kasuwar Katcha.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) mai kula da ofishin Kogi Mista Justin Uche ya shaida wa BBC cewa rashin ingantaccen tsari ya sa har yanzu ba a kai ga gano cikakkun bayanai game da fasinjojin ba.

“Matsalar ita ce, babu tsarin adana bayanin fasinjoji, don haka bayar a cikakkun bayanan fasinjojin ke da matuƙar wahala”, in ji Mista Uche.

Gwamnan jihar Kogi, Usman Ododo ya bayar da umarni ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA) ta samar da kayayyakin agaji ga iyalan mutanen da abin ya shafa,” in ji wata sanarwa daga ofishin gwamnan.

Haka kuma gwamnan ya buƙaci asibitocin da aka kwantar da mutanen da aka ceto da rai, su ba su kulawar da ta dace.

Gwamnan na Kogi ya kuma koka kan yadda ake yawan samun haɗurran a harkar sufurin ruwa a Najeriya, sannan ya buƙaci a tsaurara matakan da suka dace don ganin an kauce wa samun irin waɗannan haɗurran a nan gaba.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp