fidelitybank

An sake gano gawarwaki 54 da suka nutse a kogin Neja

Date:

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya ta ce ta gano aƙalla gawarwaki 54 a wurin da hatsarin kwale-kwalen jihar Kogi ya auku ranar Juma’ar da ta gabata.

Ana dai kyautata zaton cewa har yanzu ba a ga fiye da mutum 100 ba, yayin da aka ceto wasu 24 da ransu.

Ƙwararrun ninƙaya da masu iyo na ci gaba da neman sauran mutanen, sai dai fatan samun ragowar mutanen da rai na ci gaba da raguwa a zukatan al’umma.

Kwale-kwalen ɗauke da fasinjoji fiye da 200 ya kife a cikin ruwan Kogin Neja tsakanin jihohin Kogi da Neja da ke tsakiyar Najeriya, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa kasuwar Katcha.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) mai kula da ofishin Kogi Mista Justin Uche ya shaida wa BBC cewa rashin ingantaccen tsari ya sa har yanzu ba a kai ga gano cikakkun bayanai game da fasinjojin ba.

“Matsalar ita ce, babu tsarin adana bayanin fasinjoji, don haka bayar a cikakkun bayanan fasinjojin ke da matuƙar wahala”, in ji Mista Uche.

Gwamnan jihar Kogi, Usman Ododo ya bayar da umarni ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA) ta samar da kayayyakin agaji ga iyalan mutanen da abin ya shafa,” in ji wata sanarwa daga ofishin gwamnan.

Haka kuma gwamnan ya buƙaci asibitocin da aka kwantar da mutanen da aka ceto da rai, su ba su kulawar da ta dace.

Gwamnan na Kogi ya kuma koka kan yadda ake yawan samun haɗurran a harkar sufurin ruwa a Najeriya, sannan ya buƙaci a tsaurara matakan da suka dace don ganin an kauce wa samun irin waɗannan haɗurran a nan gaba.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp