Ana zaman dar-dar a garin Sapele da ke karamar hukumar Sapele ta jihar Delta yayin da a ranar Laraba wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shugaban matasan yankin Sapele-Okpe, mai suna Egbejule.
Ana zargin cewa, Shugaban ya je wasan kwallon kafa ne a Makarantar Firamare ta Ogodo da ke Unguwar Ajogodo, Sapele, inda ‘yan bindigar suka yi harbi da bindiga suka yi awon gaba da shi zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Mahara sun yi amfani da damar wajen yin sata yayin da matasa ke nuna adawa da sace sacen.
Lamarin da ya sanya mazauna yankin guduwa domin tsira da rayukansu yayin da matasan Ajogodo suka fito da yawansu, da safiyar Alhamis suka tare babbar titin da ta nufi makarantar firamare ta Ogodo.
Sai da sojoji suka shiga cikin gaggawa domin tarwatsa matasan.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe har yanzu bai amsa kiran da aka yi masa ba, da kuma amsa sakon da aka aika masa.