fidelitybank

An sace daliban Najeriya fiye da 1,500 – Amnesty

Date:

Kungiyar da ke fafutukar kare hakkin da Adam ta Amnesty International ta ce shekara takwas bayan da kungiyar Boko Haram ta sace ‘yan matan makarantar Chibok 276, fiye da dalibai 1,500 wasu kungiyoyi suka sace, kuma hukumomin kasar sun kasa kare su.

Amnesty International ta bayyana haka ne cikin wani rahoton da ta fitar.

Rahoton kungiyar ya ce, a cikin dalibai 276 na Chibok da aka sace, an kashe 16 kuma har yau ba a san inda 109 suke ba.

Sannan a dalilin sace daliban da ake yi an sun kulle makarantu masu yawa kuma an fara yi wa dalibai mata auren wuri.

Amnesty ta kuma ce an sace dalibai 1,500 cikin wata 22 ne, kuma har zuwa wannan lokacin akwai dalibai kimanin 120 da ke hannun wadanda suka sace su.

Cikin dalibai 102 da aka sace a makarantar gwamnatin tarayya ta Birnin Yauri, har yanzu tara na hannun masu garkuwa da su, haka kuma ba a sako daya daga cikin daliban makarantar Bethel Baptist High School ta Kaduna cikin dalibai 121 da aka sace ba.

Sannan an kashe dalibai biyar na jami’ar Greenfield ta Kaduna, kuma wani dalibin makarantar sakandaren Kankara ma ya rasa ransa. In ji BBC.

Akwai kuma dalibai biyar na makarantar Islamiyar Salihu Tanko da ke Tegina da masu garkuwa da su suka kashe, inda a karshe rahoton ya bayyana cewa daliba Leah Sharibu ta makarantar gwamnati da ke Dapchi ce kadai ba a sako ba cikin dalibai 276 da aka sace.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulÉ—a da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu É—auki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta É—aukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp