fidelitybank

An sace Dalibai 5 Mata a Katsina

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne a safiyar Laraba, sun yi garkuwa da wasu dalibai mata 5 na jami’ar tarayya da ke Dutsin-ma (FUDMA) a jihar Katsina.

Rahotanni na cewa, an sace daliban ne a gidansu da ke bayan makarantar Mariamoh Ajiri Memorial International School, daura da hanyar Tsaskiya da misalin karfe 2:30 na safe.

Majiyoyi da dama da suka hada da ma’aikata da daliban jami’ar sun tabbatar wa DAILY POST hakan.

A cewar daya daga cikinsu, ‘yan bindigar da yawansu ya kai dauke da muggan makamai, sun kai hari gidan daliban da ke kan hanyar Tsaskiya tare da yin garkuwa da su da karfi.

Shi ma jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya tabbatar da sace mutanen.

Ya bayyana cewa an kama wasu da ake zargi da hannu a lamarin.

Ya kuma kara da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin tare da samun nasarar kubutar da daliban da aka sace.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp