fidelitybank

An sace Amarya da Ƙawayen ta a Sokoto

Date:

Harin ya faru ne a ranar Asabar a kauyen Kwaren Gamba, kusa da Kuka Teke, wuri da aka saba kai hari daga kungiyoyin ‘yan bindiga da ke da alaka da Bello Turji.

Ganau sun bayyana cewa maharan sun dira yankin tare da sace mutanen, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin tashin hankali.

Wani masanin tsaro, Zagazola Makama, ya bayyana cewa al’ummar yankin suna cikin tsananin dimuwa.

Iyayen wadanda aka sace suna cikin halin bakin ciki, inda wani dattijo a kauhen ya ce, “Halinda muke ciki ya fi karfin mu, kuma mutanenmu suna rasa kwarin guiwa.”

A kwanakin baya, ‘yan bindiga sun kashe akalla mutane 10 a Jihar Sakkwato.

‘Yan bindiga sun kai hari a kauyen Dantudu Lajinge, inda suka kashe ‘yan sa-kai tara tare da sace matan su.

Wani mazaunin kauyen, Bello Dan-Tudu, ya ce, “Sun yanka mutane tara kamar awaki.”

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa an harbi mutane 10 a wuya, daya kawai ya tsira.

Shugaban karamar hukumar Sabon Birni, Ayuba Hamisu, ya tabbatar da harin da lamarin.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp