fidelitybank

An sace Ƴan Jaridu biyu da iyalan su a jihar Kaduna

Date:

Masu garkuwa da mutane sun sace ‘yan jarida biyu tare da mata da ‘ya’yansu a jihar Kaduna.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ‘yan jarida ta ƙasa, NUJ reshen jihar ta fitar, ta ce lamarin ya faru ne ranar Asabar da daddare a gidajensu a unguwar Danhono da ke yankin ƙaramar hukumar Chikun na jihar Kaduna.

Rahotonni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na dare lokacin da ‘yan bindigar suka shiga unguwar riƙe da makamai suna harbin kan mai tsautsayi.

Ƙungiyar NUJ ta kaɗu da labarin garkuwa da ‘yan jaridun biyu da ta ce suna aiki ne da jaridun ‘The Nation’ da kuma ‘The Blue Print’ da kuma iyalan nasu.

Ƙungiyar ta kuma yi Allah wadai da faruwar lamarin, tare da yin kira ga jami’an tsaro a jihar su jajirce wajen kuɓutar da su.

Jihar Kaduna na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro, inda a wasu lokuta ‘yan bindiga ke kai hare-hare tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Ko a watan Maris na wannan shekarar ma wasu ‘yan bindiga suka kai hari makarantar Kuriga da ke jihar, tare da sace ɗalibai fiye da 100, kodayake daga baya ukumomi sun kuɓutar da su bayan shafe wasu kwanaki.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp