A jiya ne aka kammala tattaunawar da shugaban kasar Senegal Macky Sall ya kira kan rikicin siyasar kasar tare da yarjejeniyar gudanar da zaɓe a ranar 2 ga watan Yuni, kamar yadda gidan talabijin na ƙasar RTS ya ruwaito.
Duk da cewa mafi yawan ‘yan adawa sun kaurace wa tattaunawar, waɗanda suka mamaye taron ƴan ƙawancen Sall ne.
Wakilai, da suke magana a RTS, sun nuna cewa ranar da aka zaɓa za ta ba da damar gudanar da zabukan bayan sallar Idi da kuma gabanin damina.
Duk da iƙirarin da Shugaba Sall ya yi na cewa wa’adinsa zai kare ne a ranar 2 ga Afrilu, mahalarta taron sun ba da shawarar ya ci gaba da aiki a matsayin shugaban ƙasar har sai an rantsar da magajinsa.
Waɗannan shawarwarin daga tattaunawar za su buƙaci amincewar shugaban kasa kafin a mika su ga Majalisar Tsarin Mulki don tabbatar da su.
Ƙasar Senegal dai ta tsinci kanta a cikin rikicin siyasa mafi muni cikin shekaru da dama bayan da shugaba Sall ya yanke shawarar ɗage zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu.