fidelitybank

An rufe kasuwannin sayar da Shanu 11 saboda ‘yan ta’addan Zamfara

Date:

Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da rufe kasuwannin shanu goma sha daya a fadin jihar.

Gwamnatin ta ce rufewar ya biyo bayan gano cewa wasu mutane na yin mu’amala da shanu ba tare da cikakkun bayanai ba kamar yadda doka ta tanada.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Mumir Haidar Kaura ya fitar.

Ya kuma kara da cewa, an sanar da rufe kasuwannin sakamakon rahotannin tsaro cewa ‘yan bindiga na amfani da kasuwannin wajen sayar da shanunsu da suka sace.

Sanarwar ta ce, kasuwannin da abin ya shafa sun hada da na Tsafe da Bilbis a karamar hukumar Tsafe da kuma kasuwar Wuya da ke karamar hukumar Anka.

“Sauran sun hada da kasuwar Magamin Diddi a karamar hukumar Maradun, kasuwar Galadi a karamar hukumar Shinkafi, kasuwar Mada da ke karamar hukumar Gusau da Sabon Birnin Danali a karamar hukumar Birnin Magaji.

Sauran kasuwannin su ne; Kasuwar Kokiya, Chigama da Nasarawar Godel, duk a cikin karamar hukumar Birnin Magaji.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin jihar ta ga ya zama dole ta rufe wadannan kasuwanni saboda rahotannin tsaro cewa ‘yan fashin na hada baki da wasu marasa kishin kasa domin sayar da shanun da suka sace a kasuwannin”.

“Gwamnatin jihar ta umurci jami’an tsaro da su tabbatar da bin doka da oda tare da kamo duk wanda ya karya dokar.

“Tun daga nan aka umarci jami’an tsaro da su kama duk wanda aka samu a cikin wadannan kasuwannin da abin ya shafa.

Haidar ya yi kira ga al’ummar jihar da su bi wannan umarni tare da ba gwamnatin jihar hadin kai a kokarinta na kawar da ayyukan ‘yan fashi a jihar.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp