An rufe filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Legas na wani dan lokaci da sanyin safiyar ranar Alhamis, 19 ga watan Mayu, bayan da aka tsinci gawar wani mutum da aka daure a kan titin jirgin sama mai lamba 18 na filin jirgin saman.
Kawo yanzu dai ba a tantance ko waye gawar ba, haka kuma, ba a iya tantance ko jirgin ne ya fado da mamacin ko kuma ya sauka a kan titin jirgin.
Sai dai jami’an filin jirgin sun bayyana cewa, an rufe titin jirgin na wani dan lokaci yayin da tawagar jami’an hukumar kula da filayen jiragen sama ta tarayyar Najeriya da rundunar ‘yan sandan Najeriya suka É—auke gawar daga titin jirgin.
A yayin rufe titin jirgin na wucin gadi, an hana zirga-zirgar jiragen sama na kasa da kasa sauka da tashi daga tashar jiragen sama na kasa da kasa.