An raunata sojoji uku tare da kashe wasu mutum shida bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a garin Ikobi na ƙaramar hukumar Apa da ke jihar Benue.
Rundunar sojin ƙasar ta tabbatar da raunata sojojinta uku bayan arangama da ‘yan bindigar waɗanda suka afka wa garin a ƙarshen mako.
Rahotonni sun ce, sojojin da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Whirl Stroke (OPWS) da ke da shalkwata a garin Agagbe sun mayar da martani bayan da suka samu labarin maharan.
Jihar Benue na daga cikin jihohin da ke fama da yawan hare-haren ‘yan bindiga masu alaƙa da ƙabilanci da addini