An rantsar da Monday Okpbhelo a matsayin sabon zaɓabɓen gwamnan jihar Edo.
Sanata Okpbhelo na jam’iyyarsa APC ya doke abokan karawarsa na jam’iyyar PDP, Barr. Asue Ighodalo da kuma na jam’iyyar Labour Olumide Akpata, a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar 21 ga watan Nuwamba.
An kuma ranstar da Hon. Denise Idahosa a matsayin mataimakin gwamnan jihar.
Alkalin alkalan jihar ne Daniel Okongbowa ya jagoranci rantsar da su.
Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan jihar mai barin gado, Godwin Obaseki bai halarci taron rantsuwar ba.