fidelitybank

An rantsar da sababbin Alkalai 8 a Adamawa

Date:

Gwamnatin jihar Adamawa ta rantsar da sabbin alkalai takwas da aka nada.

A ranar Juma’a ne babban alkalin jihar, Mai shari’a Nathan Musa ya rantsar da alkalan da aka kara daga kotunan yankin.

A yayin bikin wanda ya gudana a harabar babbar kotun da ke babban birnin jihar, Yola, Mai shari’a Nathan Musa, ya bukaci sabbin alkalai da su yi aiki tukuru bisa ka’idojin da aka gindaya.

Sabbin alkalan kotun guda takwas sun hada da Barista Aliyu Ahmed, Ibrahim Aliyu, Abubakar Habu, Joseph Mafa, Usman Adamu Laido, Bashir Musa, Ibrahim Yusuf da Umar Hamman Audi.

Mai shari’a Nathan Musa ya tunatar da alkalan kotunan kolin shari’a, ya kuma gargade su da su guji nuna son zuciya da rashin sanin yakamata, inda ya kara jaddada aniyar bangaren shari’a na jiha na yin gwagwarmayar tabbatar da adalci da kuma tabbatar da tsafta a bangaren shari’a.

Daya daga cikin sabbin alkalai da aka rantsar, Barista Joseph Mafa wanda ya yi jawabi ga dukkaninsu, ya yabawa babban alkalin da ya same su a matsayin wadanda suka cancanta a matsayin su.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp