fidelitybank

An rantsar da mai shari’a mace a karo na farko a Pakistan

Date:

A karo na farko an rantsar da mai shari’a a Kotun Kolin Pakistan a babban birnin kasar Islamabad.

Ayesha Malik, mai shekara 55, yanzu za ta rinka zama tare da sauran alkalai maza 16 a babbar kotun kasar mai rinjayen Musulmi.

Lauyoyi da masu raji sun bayyana nadin da cewa wata nasara ce ta daban bayan gwagwarmaya ta gomman shekaru ta ganin an samu wakilcin mata a kasar ta Pakistan wadda maza suka mamaye kusan komai.

Sai dai wasu lauyoyin da alkalai sun soki nadin Ayesha saboda ba ta kai wasu daga cikin ‘yan takarar mukamin ba a matsayi.

Kungiyar kare hakkin dan-Adam ta Human Rights Watch ta ce Pakistan ce kasar Asia daya da ba a taba nada wata mace a matsayin mai shari’a a Kotun Koli ba.

Haka kuma kashi hudu cikin dari ne kawai na alkalan kasar mata.

Ayesha wadda ta yi karatu a kwalejin koyon aikin lauya ta Pakistan da Jami’ar Harvard ta Amurka, ta yi aiki a a matsayin babbar mai shari’a a birnin Lahore da gabashin Pakistan tsawon shekara 20.

Ana ganin ta taka rawa sosai wajen kalubalantar shari’o’i da maza ke danniya a lardin.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp