fidelitybank

An nada wanda zai binciki shugaban kasar Amurka

Date:

Babban mai shigar da kara na gwamnatin Amurka, Merrick Garland, ya nada wani jami’i na musamman domin ya binciki Shugaban Amurka, Joe Biden, kan badakkalar wasu takardun sirri mallakin gwamnati da aka gano a ofisoshinsa.

Robert Hur wanda tsohon babban jami’in ma’aikatar shari’a ne a karkashin gwamnatin tsohon Shugaba Donald Trump, shi ne zai jagoranci binciken.

A makonnin da suka gabata, na gano wasu takardun gwamnatin Amurka na sirri cikin wani ofishin da Shugaba Biden yayi amfani da shi bayan ya sauka daga mukamin mataimakin shugaban kasa a gwamnatin Barack Obama.

Fadar White House ta sanar cewa za ta hada kai sosai da mai binciken.

Gano wadannan takardun ya kasance wani abin kunya ga Mista Biden, ganin cewa ba a jima ba da tsohon shugaba Trump ma ya fuskanci irin wannan binciken.

Ranar 2 ga watan Nuwambar bara aka gano takardu na farko a wata cibiya mai suna Penn Biden Center, wadda mallakin Shugaba Biden ce da ya kaddamar a birnin Washington DC. An dai mika dukkan takardun ga gidan adana takardu na gwamnatin kasar, wato National Archives, kamar yadda Mista Biden ya sanar da kansa.

Mista Garland ya ce an kuma gano wasu takardun na daban ranar 20 ga watan Disamba a gidan Shugaban Amurkar da ke Wilmington na Jihar Delaware, kuma ya kara da cewa a safiyar Alhamis da ta gabata, lauyoyin Mista Biden sun kira masu bincike domin sanar da su cewa an gano karin wata takardar ta sirri a wani gidan Mista Biden din.

Bayan wani kwarya-kwaryan bincike ne da babban lauyan gwamnati John Lausch ya gabatar, Mista Garland ya ga ya dace a nada mai bincike na musamman domin ya bincike yadda Shugaba Biden ya mallaki wadannan takardun sirrin.

Yayin wata ganawa da yayi da manema labarai da safiyar Alhamis, Mista Biden ya sake nanata maganar da yayi cewa lauyoyinsa sun sanar da jami’na ma’aikatar shari’a dukkan abubuwan da suka gano, kuma ya dauki batun da muhimmanci sosai.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp