Gwamnatin tarayya ta amince da nadin Mista Anamekwe Chukwunyere Nwabuoku a matsayin mai kula da ofishin Akanta-Janar na Tarayya (OAGF), biyo bayan binciken da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) na Babban Akanta Janar na Gwamnatin Tarayya, Ahmed Idris.
Hakan na kunshe ne a cikin wata takarda mai dauke da kwanan watan 20 ga Mayu, 2022 mai dauke da sa hannun Aliyu Ahmed, Babban Sakatare (Kudi), Ma’aikatar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare na Kasa.
Wasikar ta ce nadin yana jiran sakamakon binciken.
A wannan matsayi, ana sa ran Mista Anamekwe zai gudanar da aikinsa bisa bin ka’idojin da kuma kiyaye mafi girman kwarewar da ake sa ran jami’in da ke aiki a matakinsa.
Mista Anamekwe yana da Higher National Diploma (HND) a Accountancy a Institute of Management and Technology (IMT) Enugu, da Master of Science (M.Sc) a fannin sarrafa kudi daga Jami’ar Common Wealth da ke Belize.