fidelitybank

An mayar da batun kudirin haraji siyasa – Sanata Abba Moro

Date:

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattijai, Sanata Abba Moro, ya nuna damuwa kan yadda tattaunawar kan shirin gyaran haraji a Najeriya ke kawo rarrabuwar kai.

Sanata Moro ya yi kira da a mayar da hankali wajen yin cikakken nazari kan kudirin gyaran harajin ba bangaranci ba.

Ya jaddada muhimmancin daukar mataki kan korafe-korafen masu ruwa da tsaki, ciki har da la’akari da tasirin doka na sauran bangarorin da ke damun yan Najeriya.

Daga cikin matsalolin da aka fi magana a kansu akwai canje-canje da ake so a yi kan tsarin rarraba VAT, wanda masu sukar suka ce zai iya cutar da yan Arewa.

“Idan aka gabatar da tsarin samun VAT kamar yadda yake a kudirin, ana iya ganin cewa hakan zai saba wa kundin tsarin mulki domin babu tanadin hakana  tsarin mulki,” in ji Moro.

Ya lura cewa daga shafukan sada zumunta da wallafe-wallafe na baya-bayan nan, tattaunawar ta dauki salo na siyasa, tana neman raba kawunan yankunan Arewa da Kudu.

“Ina so in ce cewa wannan siyasantar da aka yi wa kudirin ne a farko ya kawo mu inda muke yanzu, don haka ba zan duba bangaren siyasa na batun ba. Ina ganin cewa idan aka kara wayar da kai da bayyana muradun kudirin, yawancin mutane da ba su fahimci batun ba, za su gane cewa kudirin yana da manufar alheri ga Najeriya baki daya,” in ji shi.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp