fidelitybank

An mayar da batun kudirin haraji siyasa – Sanata Abba Moro

Date:

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattijai, Sanata Abba Moro, ya nuna damuwa kan yadda tattaunawar kan shirin gyaran haraji a Najeriya ke kawo rarrabuwar kai.

Sanata Moro ya yi kira da a mayar da hankali wajen yin cikakken nazari kan kudirin gyaran harajin ba bangaranci ba.

Ya jaddada muhimmancin daukar mataki kan korafe-korafen masu ruwa da tsaki, ciki har da la’akari da tasirin doka na sauran bangarorin da ke damun yan Najeriya.

Daga cikin matsalolin da aka fi magana a kansu akwai canje-canje da ake so a yi kan tsarin rarraba VAT, wanda masu sukar suka ce zai iya cutar da yan Arewa.

“Idan aka gabatar da tsarin samun VAT kamar yadda yake a kudirin, ana iya ganin cewa hakan zai saba wa kundin tsarin mulki domin babu tanadin hakana  tsarin mulki,” in ji Moro.

Ya lura cewa daga shafukan sada zumunta da wallafe-wallafe na baya-bayan nan, tattaunawar ta dauki salo na siyasa, tana neman raba kawunan yankunan Arewa da Kudu.

“Ina so in ce cewa wannan siyasantar da aka yi wa kudirin ne a farko ya kawo mu inda muke yanzu, don haka ba zan duba bangaren siyasa na batun ba. Ina ganin cewa idan aka kara wayar da kai da bayyana muradun kudirin, yawancin mutane da ba su fahimci batun ba, za su gane cewa kudirin yana da manufar alheri ga Najeriya baki daya,” in ji shi.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp