fidelitybank

An matasawa kotu ta kori Hannatu Musawa a matsayin Minista

Date:

Wata ƙungiyar farar-hula da ake kira ‘Incorporated Trustees of Concerned Nigerians’ ta kai sabuwar ministar raya al’adu, Hannatu Musa Musawa Kotu inda ta buƙaci a soke naɗin da aka yi mata.

Ƙungiyar ta kare manufofinta kan bukatar hakan, saboda korafe-korafen da suka biyo bayan gane cewa ministar ba ta kammala aikin yi wa ƙasa hidima ba wato NYSC.

Masu shigar da karar karkashin jagorancin Deji Adeyanju sun buƙaci kotu ta duba kundin tsarin mulkin ƙasa ta fayyace musu idan mutum na iya haɗa aikin hidimar ƙasa ta NYSC da kuma muƙamin minista a lokaci guda.

Sannan sun buƙaci a ci tarar ministar naira miliyan 100 da kuma naira miliyan ɗaya kuɗin ɓata lokaci a kai ta kotu.

Takardun da suka miƙawa kotu mai shafi 13 sun kuma bayyana cewa, Hannatu Musawa ta amsa cewa yanzu take NYSC ɗinta, kuma an tura ta Abuja domin hidimtawa ƙasa.

Korafin nasu na jadadda cewa babu dokar NYSC da ta amince mai hidimatawa ƙasa ya karɓi wani aiki na gwamnati ko muƙamin siyasa.

Ƙungiyar ta ce ya zama wajibi a yi adalci wajen wannan shari’a.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp