Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC ta ce kusan akwatin zabe 800 da rumfunan zabe 200 aka lalata yayin wani hari da aaka kai wa ofishinta da ke Jihar Anambra.
Wannan harin na zuwa ne kasa da wata guda gabanin a gudanar da babban zabe na kasar.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya a Jihar ta Anambra ta ce wasu ‘yan bindiga ne suka kai wannan harin kan ofishin nata da ke Ojoto cikin karamar hukumar Idemili South da sanyin safiyar ranar Laraba cikin wasu motoci hudu da ba a sanya wa lamba ba.
Karanta Wannan:Â Karancin man fetur zai kawo mana cikas – INEC
Kakakin rundunar Tochukwu Ikenga ya ce bayan maharan sun isa wurin sai suka jefa wasu abubuwa masu fashewa, kana daga baya suka kai wa ofishin ‘yan sandan da ke yanki tare da wani gida duka a kusa da ofishin hukumar zaben.
Sanarwar da ‘yan sanda ta fitar na cewa wani matashi ya rasa ransa sannan wani mutumin na daban ya sami raunuka inda aka tafi da shi asibiti.