fidelitybank

An kwace Baburan Achaba 1,292 a Abuja

Date:

Sashen kula da tsaftace muhalli na Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA) ya rusa gine-gine 3,197 da aka gina ba bisa tsari ba sannan ya markade babura 1,292 a cikin kwanaki 14 da suka wuce.

Shugaban wannan sashe Shehu Ahmad ya sanar da haka a taron da ya yi da manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Ahmad ya ce hukumar ta yi haka ne domin kara tsaftace muhalli sannan da samar da tsaro wa mutane a Abuja.

“ Mun rusa gine-gine 123 da aka gina ba bisa ka’ida ba a Katampe Extension da Guzape sannan muka rusa bukkoki 3,074 a Durumi I, II, III, Monkey Village, Dagba, sansanin ‘yan gudun hijira dake Durimi da wasu matsugunan da aka gina su a karkashin gadoji a Abuja.

“ Daga nan kuma mun lalata babura 1,292 da muka kama a sassan Abuja da doka ta hana ‘yan achaba aiki.

Ya ce hukumar ta yi duk wadannan aiyuka ne daga ranar 9 zuwa 22 ga Disambar 2022.

Ya ce Guzape, Katampe Extension, Durumi, Wasa, Kuchi Goro da Lugbe hanyar tashar jiragen sama na daga cikin wuraren da suka rusa gine-gine da aka kafa ba bisa doka ba.

Sannan hanyar tashar jiragen sama, Durumi, Kubwa, Asokoro Extension da Guzape na daga cikin wuraren da suka kama babura.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp