Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, WTO ta sake zaɓar Dakta Ngozi Okonjo-Iweala a matsayin shugabanta a wa’adin mulki na biyu, inda za ta ci gaba da jagorantar ƙungiyar har zuwa 2029.
Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da harkokin cinikayyar duniya ke cikin wani mawuyacin yanayi.
A farkon makon nan zaɓaɓɓen shugaban Amurka, Donald Trump ya ce zai ƙaƙaba sabbin haraje-harajen cinikayya da ƙasashen Canada da Mexico da China idan ya kama aiki cikin watan Janairu.
A lokacin wa’adin mulkinsa na farko, Donald Trump ya yi yunƙurin hana Ms Okonjo-Iweala samun matsayin, inda ta samu nasarar ɗarewa muƙamin bayan Joe Biden ya zama shugaban Amurka.
Babban abin tambaya a yanzu shi ne irin tasirin da ƙungiyoyin kasuwanci irin WTO za su yi, a daidai lokacin da manyan ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki ke ƙara samun saɓanin kasuwanci.
Ga kuma batun yaƙin Ukraine da ya haifar da ƙarin takunkuman kasuwancin tsakanin wasu manyan ƙasashe.