fidelitybank

An kuma yin garkuwa da mutane 15 a Kaduna

Date:

A ranar Asabar din da ta gabata ne wasu ‘yan ta’adda suka kai hari kan al’ummar Dogon-noma da ke karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna, inda suka yi garkuwa da mata 15 da namiji guda.

Wani mazaunin kauyen mai suna Istifanus, ya shaidawa manema labarai cewa da yawa daga cikin mazauna kauyen sun gudu zuwa yankunan da ke makwabtaka da su domin tsira da rayukansu a lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari tare da harbe-harbe.

“Za mu iya tabbatar da adadi da yamma lokacin da za mu iya shiga ƙauyen. Maharan sun mamaye kauyen ne da misalin karfe 5:30 na safiyar ranar Asabar din nan da yawan gaske, inda suka rika harbi ba kakkautawa.

Wani tsohon shugaban karamar hukumar, Cafra Caino ya ce ba za a iya tantance adadin wadanda suka mutu ba.

“Har yanzu ba mu sami adadin wadanda suka mutu ba saboda mutanen yankin sun yi gudun hijira a lokacin da maharan suka mamaye al’umma. Al’ummar, wani lokaci a shekarar 2019, sun fuskanci mummunan hari inda aka kashe mutane 74 kuma a baya-bayan nan al’umma na fuskantar hare-hare,” inji shi.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yan sandan ta kasa samun martani kan lamarin.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp