fidelitybank

An kuma daure tsohon Firaministan Pakistan na shekaru 14

Date:

An yanke wa tsohon firaministan Pakistan, Imran Khan da matarsa ​​Bushra Bibi hukuncin ɗauri na shekara 14, hukunci na biyu da aka yanke wa tsohon Firaministan cikin kwana biyu.

An samu ma’auratan da laifin cin gajiyar kyautukan gwamnati ba bisa ka’ida ba – mako guda kafin babban zaben da aka hana shi tsayawa takara.

Khan, wanda abokan hamayyarsa suka hamɓarar da shi a matsayin firaminista a shekarar 2022, ya riga ya yi zaman gidan yari na shekaru uku bayan samun shi da laifin cin hanci da rashawa.

Ya ce yawancin ƙararrakin da ake yi masa bita da kullin siyasa ne.

Shari’ar ta ranar Laraba ta shafi tuhume-tuhumen da ake yi masa ne a kan wasu kyaututtukan gwamnati da aka yi masa da matarsa ​​a lokacin da suke kan karagar mulki, yayin da kuma shari’ar ta ranar Talata – wadda aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kan zargin fallasa wasu bayanan sirri na ƙasar.

Ana tunanin hukunce-hukuncen biyu za su gudana a lokaci guda, kodayake ba a tabbatar da hakan ba.

Kotun ta kuma umarci ma’auratan da su biya tarar kuɗi rupe biliyan 1.5, dalar Amurka 5.3m ke nan.

Lauyoyin Khan sun ce za su daukaka kara zuwa babbar kotun Pakistan kan shari’o’in biyu.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp