fidelitybank

An kuma cafke Dan Bindiga yayin tafiya aikin Hajji

Date:

Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, sun bayyana cewa sun kama wani dan fashi da makami mai garkuwa da mutane a Sokoto yayin da ake tantance maniyyata mahajjata.

Wanda ake zargin, kamar yadda Aminiya ta ruwaito, mai suna Sani Galadi, an kama shi ne a ranar Litinin a filin jirgin saman Sultan Abubakar da ke Sakkwato, bayan da jami’an ā€˜yan sanda suka bi shi.

Kamen na zuwa ne kimanin sa’o’i 24 bayan da jami’an tsaro suka kama wani da ake zargin dan fashi da garkuwa da mutane ne a sansanin alhazai da ke Abuja.

Wanda ake zargin, mai suna Yahaya Zango, an bayyana cewa yana da alaka da sace-sacen mutane da dama a Abuja da Kogi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne jami’an tsaro da suka hada da na DSS suka cafke Zango a yayin da ake tantance maniyyatan da suka nufa.

Idan za a iya tunawa, a ranar 12 ga watan Mayu, NAHCON ta kammala jigilar maniyyata mahajjata a jihohi hudu zuwa kasar Saudiyya, yayin da ake sa ran ā€˜yan Najeriya 64,188 za su halarci aikin hajjin bana.

Babban hafsan hafsoshin tsaron kasar, Christopher Musa, a ranar Juma’a, ya ce sojoji sun sayo sabbin kayan aiki domin karfafa ayyukan yaki da rashin tsaro, ciki har da sake bullar hare-haren ā€˜yan tada kayar baya.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alʙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Ę“an ʙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maʙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ʙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ʙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaʙulo gawar...
X whatsapp