Jamiāan hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, sun bayyana cewa sun kama wani dan fashi da makami mai garkuwa da mutane a Sokoto yayin da ake tantance maniyyata mahajjata.
Wanda ake zargin, kamar yadda Aminiya ta ruwaito, mai suna Sani Galadi, an kama shi ne a ranar Litinin a filin jirgin saman Sultan Abubakar da ke Sakkwato, bayan da jamiāan āyan sanda suka bi shi.
Kamen na zuwa ne kimanin saāoāi 24 bayan da jamiāan tsaro suka kama wani da ake zargin dan fashi da garkuwa da mutane ne a sansanin alhazai da ke Abuja.
Wanda ake zargin, mai suna Yahaya Zango, an bayyana cewa yana da alaka da sace-sacen mutane da dama a Abuja da Kogi.
A ranar Lahadin da ta gabata ne jamiāan tsaro da suka hada da na DSS suka cafke Zango a yayin da ake tantance maniyyatan da suka nufa.
Idan za a iya tunawa, a ranar 12 ga watan Mayu, NAHCON ta kammala jigilar maniyyata mahajjata a jihohi hudu zuwa kasar Saudiyya, yayin da ake sa ran āyan Najeriya 64,188 za su halarci aikin hajjin bana.
Babban hafsan hafsoshin tsaron kasar, Christopher Musa, a ranar Jumaāa, ya ce sojoji sun sayo sabbin kayan aiki domin karfafa ayyukan yaki da rashin tsaro, ciki har da sake bullar hare-haren āyan tada kayar baya.