fidelitybank

An kubutar da Fasinjoji 12 na jirgin kasar Edo

Date:

Hukumomin jihar Edo, ta ce, an kuɓutar da fasinjoji 12 na jirgin ƙasa, da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a tashar jiragen ƙasa da ke jihar a makon da ya gabata.

An kama wasu daga cikin ‘yan bindigar da suka yi garkuwa da su, to sai dai wasu daga cikinsu sun tsere tare da wasu fasinjojin biyu a lokacin da jami’an tsaro ke ƙoƙarin kuɓutar da su.

Hukumomin jihar sun ce an kuɓutar da mutanen 12 a lokacin da jami’an tsaro suka yi wa masu garkuwa da mutanen kwanton ɓauta.

Tuni aka kai mutanen da aka kuɓutar ɗin asibiti domin duba lafiyarsu.

Gwamnatin jihar ta alƙawarta ci gaba da nemo sauran fasinjojin biyu da ke hannun ‘yan bindigar.

Gwamnan jihar ya soki hukumar kula da sufurin jiragen ƙasa ta ƙasar kan gaza samar da tsaro kan tasoshin jiragen ƙasan duk da faruwar makamancin wannan hari a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar a shekarar da ta gabata.

Tun da farko dai hukumomin sun ce mutum 32 ne ‘yan bindigar suka yi garkuwa da su a harin da suka kai tashar jirgin ƙasa ta Igueben a makon da ya gabata, to sai dai daga baya hukumomin sun ce adadin mutanen 20 ne.

An saki mutum shida a farkon makon nan a wani samame da jami’an tsaro suka kai wa ‘yan bindigar.

Kama mutane domin neman kuɗin fansa ba sabon abu ba ne a Najeriya, lamarin da ya zama ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen tsaro a ƙasar a ‘yan shekarun baya-bayan nan.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp