fidelitybank

An kuɓutar da Matar Basaraken da aka kashe tare da kama mutane 13

Date:

An kubutar da matar basaraken gargajiyar da aka kashe, marigayi Oba Olusegun Aremu-Cole wanda aka kashe a fadarsa ranar Alhamis.

An dai yi garkuwa da mai dakin nasa a ranar Alhamis da daddare tare da wata mata guda. wanda ba a tantnace ko wace ce ba, a ƙaramar hukumar Ekiti ta jihar Kwara.

An kuɓutar da su ne a daren ranar Litinin kuma sun isa garin Koro da misalin karfe 10:45 na dare.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, Ejire-Adeyemi Toun, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Ko da yake bai bayyana sunan mutum na biyu da aka kubutar ba, rahotanni sun ce ’yar sarauniyar ce.

A cewar kakakin rundunar ‘yan sandan, aikin ceton ya biyo bayan wani aikin hadin gwiwa da jami’an hukumar tsaron farin kaya (DSS) da ‘yan sanda da sojoji da ‘yan banga da mafarauta suka yi.

Ya ce jami’an tsaro sun kutsa cikin dajin da ke tsakanin jihohin Kwara da Ekiti bayan da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin tura wani jirgin sama na ‘yan sanda domin binciken cikin dajin.

“Wannan aiki ceton ya kai ga nasarar ceto matar marigayin da kuma wani mutum daya a ranar 5 ga watan Fabrairun 2024.”

Sanarwar ta kara da cewa tuni aka haɗa waɗanda aka kuɓutar din da iyalansu, cikin jin dadi.

“A ci gaba da binciken, Sufeto Janar na ‘yan sanda IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya amince da tura jami’an ‘yan sanda ta jirgin sama domin bincike ta sararin samaniya domin taimaka wa Kwara da jihar EkitiI.”

Ejire-Adeyemi ya kara da cewa, “aikin ceton ya kuma kai ga kama wasu maza 13 da ake zargi da hannu a yanzu haka.”

“Wadanda aka kama dai suna fuskantar tambayoyi masu karfi da nufin taimakawa wajen cafke ‘sauran mutanen da ke da alhakin kai harin baki daya.”

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp