fidelitybank

An kuɓutar da ‘ya’yan ɗan majalisar Zamfara bayan wata 17 da sace su

Date:

Ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro tare da hadin gwiwar ƴan sanda sun ceto ‘ya’ya mata biyu na wani ɗan majalisar jihar Zamfara da aka yi garkuwa da su wata 17 da suka gabata.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa a ranar Talata ne aka miƙa yaran biyu, Maryam da Nana Asma’u ga mahaifin nasu Aminu Ardo a hedikwatar ƴan sanda ta ƙasa da ke birnin Abuja.

A lokacin miƙa wa ɗan majalisar ‘ya’yan nasa, mataimakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Isuku Victor ya ce mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro Mallam Nuhu Ribaɗo ne ya jagoranci ƙoƙarin ceto yaran tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro.

A watan Nuwanbar 2022 ne ƴan bindiga suka kai hari gidan Aminu Ardo a Jangebe da ke jihar Zamfara tare da yin garkuwa da matarsa da kuma ƙananan yaransa huɗu.

Mahaifiyar yaran da kuma biyu daga cikin yaran sun samu kuɓuta bayan da rahotonni sujka ce sun gudu daga inda [‘yan bindigar suka tsare su, inda suka bar sauran biyun Maryam da Nana Asma’u a hannun masu garkuwar.

CSP Victor ya ce yaran sun fuskanci wahalar rayuwa a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan bindigar ciki har da shan ruwan rafuka.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp